Saturday, December 8, 2012

wakar Begen Muhammadu Daga Malam Nasiru Kabara

wannan waka ce da marigayi Malam Nasiru Kabara ya rubutu, domin nuna tsantsar kaunarsa ga Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wassallam. Wakar Begen Muhammad ta Malam Nasiru Kabara Bismillahir Rahmanir al Rahim Wa sallalLahu ala nabiyul karim 1. Begen Muhammadu ya cika mani zuciya acikinta ba sauran muhalli ko daya. 2. Wallahi garwashin bidar sado da shi ya kona sassan zuciya wayyoniya 3. Naso ka Daha kamar ido ga makauniya naso inje ni gareka koda sau daya 4. Naso ziyara gani bani da fiffike kaka nake na gano masoyin zuciya 5. Na so ka son mai wabiya da ta so diya ko ko maridhi yadda yaso lafiya. 6. Ko san abincin nan ga wanda ya yunwata ko ko ruwa ga maji kishi zai sha wuya. 7. Mukhtari ka tafi ban gane ka a duniya kona rabauta inga ko gun kwanciya 8. Acikin mafarki in na samu sai ince “Allahu Akbar uh uhum wayyo niyya” 9. Begenka ya konan kasha har jijiya Naman jikina ya zangwanye bai daya 10. Ya kona hanta har da hanjaijai duka Ya bar hawayen zuciya da idaniya 11. Kaunarka ta kone bukatar zuciya Duk babu sauran ma bukatar duniya 12. Inma akwai sauran bukatar zuciya sai ko ganinka da yamma ko ko safiya 13. Ta yada zancen duniya tatsuniya ta dauki amri wanda ya zam gaskiya. 15. Ta yada zancen zo mu ji ta dake fadi ta kalmashe gizo ta hana masa kokiya 16. Duk zuciyar da ta so ka Daha da gaskiya wallahi ta arzurta ba sauran tsiya 17. Tai sutura, ta tufata aluni bam-da-bam labudda tai shaani irin na hawainiya 18. Wata safiya yayi murmushi wata safiya Riga fara, wata ran ya sanyo shudiya. 19. Wata ran da alkyabba fara, wata ran kuwa ya fashe da kuka nai kamar dan saniya . 20. Kaka ni kai da gani cikin nan duniya wa zani kara gunsa ni wayyo niya 21. Ko nayi kara babu mai ji ko ya zam kukan amale nake, ace ko jiniya 22. Mukhtaru ka faku ga gani nasa yai wuya balle ince masa Daha ni na sha wuya 23. Shine abin kara gareshi gani nasa ya zam kamar koyin farar hankakiya 24. Dan san ganinsa yana da yar farkar wuya na dauki jure so ina ta dawainiya 25. In babu wanda nake da shi zai taimaka na sauke kayan zo taya min dauriya 26. Ni dai ganin Makka a bukatar zuciya inje ni can in samu saukin zuciya 27. Inje mahaifatai in san guri inje insha ruwan zamzam inai wata gewaya 28. Inje Safa, inje ni Marwa in dawaya inje musallai, in ziyarci mazan jiya 29. Sannan in dawo in dawafin salama bayan makaman nan da Daha ya tsaitsaya 30. In wo hajjina kamila in masgaya ni dai nufina gun mazajan gaskiya 31. Koda ina yan rarrafe in ja jiki inje Madina garin Habibi Anbiya 32. Inje ni raudhar nan ta Daha in sunkuya in gaisuwa, in dada da safe in dawaya 33. Ya Rabbi domin Anbiya’I da Auliya Domin sahabban wanda ya cika duniya 34. Ka bani iko nai ziyarar Anbiya’a dan Kudubu, dan Gausu, domin anbiya 35. A Ka saukake hanyar zuwanmu Idaibatu Dan Mujtabai, dan Ni’ima domin Ma’iya 36.Kai agajinka A Rabbu dubi idaniya Domin Tijjani al Khudubu mai Tijjaniya 37. Dan gimbiya tasa na kira ka A Rabbana Ka jikan masoyan Daha, rana da safiya 38. Ganar dani Mukhtari Daha Alaniya Domin ya kore min shuunin Duniya 39. Dauke hijabi Rabbana in gane shi fai nan duniya ya rabbi ko a manamiya 40. Rahmarka ta gama kowanne balle niya da na dauka karata ilaika Ilahiya 41. Ya Rabbi nai kara gareka fa kai daya bayanka waye zaya amsa du’a’I’ya. 42. Ka yi wo salati ga Daha kai Taslimiya a gareshi ya Rabbil wara, ya Bariya 43. Duk sanda mai bege yace ‘kul’ safiya sallu ala Mukhtaru koda sau daya 44. Aufan zuwa Tashdiri fi takmilihi Begen Muhammadu ya cika min zuciya