Thursday, April 5, 2007

Wakar Zuwa Birnin Kano; Daga Aliyu Dansidi Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau Aliyu Dan Sidi shahararren Sarkin ne a Arewacin Nigeria, yayi fice saboda irin fasaharsa da illiminsa, shi kuma ne sarkin Zazzau na farko da Turawa suka nada. Turawanne kuma suka sauke shi, bayan sun samu sabanin ra'ayi akan wasu sauye-sauyen zamani. Ya zama sarki yana da Shekara Sitiin da hudu (64), yayi sarautar Zazzau daga 1903-1920 . Jikan Sarkin Zazzau Musa ne, Bamalli. Wani abin sha'awa gameda da tarihinsa shine, shi dai bai taso a gidan Sarautar Zazzau ba, ya taso a gidan malanta ne, a hannun malaminsa Limamin Durum wato malam Abubakar. Ya taba samun sabani da Sarkin Zazzau Kwasau (Mai kogin Jini dan Sambo), wanda hakan ya sanya bar Kasar Zazzau, ya shiga yawace-yawace, inda har ya Zauna a kasar Kwantagora a zamanin Sarkin Kwantagora Ibrahim Nagwamatse. Ya wallafi wakoki da dama, cikinsu kuwa akwai Tabarkoko, Saudul Kulubi, Wakar Diga da kuma wannan waka ta Birnin Kano.
Ance wannan waka yayi tane, yayi wata Dabar bankwana da Sarakunan Arewacin Nijeriya suka shiryawa Gwamna Arewacin na Zamanin Turawa wato sir Hugh Clifford, a Birnin na Kano acikin shekara 1914. A zamaninsa akan masa kirari da "Aliyu na Awwa mai iya Sarki" . Sarkin Zazzau Aliyu dan Sidi Batijjane ne na kwarai, domin mun kawo muku wakarsa da yayiwa Shehun Darikar ta Tijjaniya wato Shehu Ahmad Tijjani, ga mai so sai ya duba cikin kudayen Turaka wato Archives. Ga dai Malam Aliyu dan Sidi a Birnin Kano.






Muna gode Allah da yayi nufi
Yasa muka taru a kofar Kano

Muna yin Salati bisa ga Muhammad
Dalilinsa anka yi mu akayi Kano

Mu kara salati bisa ga sahabbai
Mu sami dalilinsu komi anu

Zama hali ma nahnu shi muka zance
Da niy yi shiri zani birnin Kano

Diya min Muharram ga ran Lahadi
Na hau bisa jirgi zuwa na Kano

Ga Chalawa ni kwana guda muka tashi
Muna gaisuwa da dawakan Kano

Dawaki na baki kaza yan gari
Fa har muka sadu da Sarkin Kano

Da fa muka gaisa ya juya na bishi
Dada har ya kaini masauki Kano

Ina gaida masu zuwa daga nesa
Da shaihu na Kukawa ga shi Kano

Da Mahoni Laraba Gaidan Kano
Kaza Lamido Adamawa a birnin Kano

Katagum, Hadejia, kaza duk da Gombe
Misau Jama'are a birnin Kano

Da Zazzau da Bauchi, kaza Katsina
Da Daura, Gumel gasu birnin Kano

Kazaure da kau Sakkwato har da Gwandu
Kabawa da Argungu birnin Kano

Mutan Gwadabawa da Kwanni da Yabo
Gamuwa da Anka a birnin Kano

Da Meri da Augi mutanen Yamma
Mutan Jega ga su a birnin Kano

Mutan Wukari, mutanen Ibi
Da Loko da Lokoja a birnin Kano

Da Yawuri har Kwantagora Rijau
Mutan Wushishi da Bussa a Birnin Kano

Kushurki da Kunguna har Kuriga
da Gwari na Waki a taron Kano

Mutanen Maginga mtan Kanbuwa
Na Sulame gasu a birnin Kano

Illori, Nufawa, Lafai, Agaye
Fa hatta Abuja a birnin Kano

Fa har Tunkiya gata ga Damisa
Mashayansu dai sunyi kiwo Kano

Kutawa mutanen Kafi, Lafiya
Da jam'an ta Baroro a birnin Kano

Da Mahmudu Ningi da Sarkin Bura
Da Sarkin na Bassa a birnin Kano

Ina gaida Sarkin Kano Yayi Aiki
da anka yi taro garinsa Kano

Gidaje na sabka dada har liyafa
Da taryan sarakai su sabka Kano

Da sabkan farare da sabkan bakake
da birni da kauye a birnin Kano

dalili gareni in san yayi aiki
Zama nayi ko da nika je Kano

Da shi da ya sabkar da su masu sabka
Ta'ala shi bamu sawaba Kano

Fa naje da yare iri da yawa
Da busa da ganga a taron Kano

Fitawa da doki dako Feluwa
Da sayi suna sukuwa nan Kano

Mutane da doki da niz zo dasu
jimillansu hamsa zuwana Kano

Kurama, Katab har da Cawai duka
Fa duk sunyi wasa a taron Kano

Da Jaba da Gwari mutan Rumaya
Kadara fa na kai su taron Kano

Ga babban suka na dawakan saraki
Na Zazzau fa sun ka ci taron Kano

Da anka yi wasa fage ya hadu
Muhudanmu sun yi ado nan Kano

Ka rarra, ka Kabra, ku san tumkiya
Bata iya kabra ba Kano

Da tauri da tsauri idan anka goga
Guda sai shi yanke guda a Kano

Ba'an gwada karfe ba, sai inda karfe
Duwatsu fashewa su kai a Kano

Ka zaga Kano har kasan dan Kano
Na birnin Kano wanda yasan Kano

Ka kau tambaye shi tsakani da Allah
Ya bayyana maka taron Kano

Na yawata Kano gani ga dan Kano
Dada har nasan anguwa a Kano

akwai anguwan madawkin Kano
Da sunanta Yola a birnin Kano

Daneji, da Soron dinki akwai su
akwai Lungunawa da Sheshe Kano

Da Marmara duk unguwa ce duka
da Kunduke Kwankwaso duk a Kano

Akwai Wudilawa akwai Na'ibawa
Da Ibadi Fasa-keya a birnin Kano.

Caranci, Gudundi, akkwai Jarkasa
Makankari, Garko duk a Kano

Kusura, Kudancin Kano da Wazirci
Da Siradi akwai ta Kano

Karofi na Wanka da Shuni akwaisu
Madatai da Daushi akwai su Kano

Karofi na Sudawa, Zangon Ciki
Da Dandago, Diso akwai su Kano

Akwai unguwar Durunmin Kaigama
Da Bulbulas, Guntu akwai su Kano

Da Yalwa da Dala, Madaboo duka
Suna nan Arewa da Kurmin Kano

Akwai wata ko unguwa Masaka
Da Sarari da Sagagi Birnin Kano

Awai unguwa Waitaka a Kano
Akwai Durumin Dakata min Kano

Mahanga, Kutumbawa duk unguwa ce
Da Damtsenka Tsage a Birnin Kano

Akwai Cediya ta Kuda unguwa ce
Akwai Kalaman Dusu duk a Kano

Da Lallokin Lemu, da kau Makwarari
Makwalla fa duk unguwa ce Kano

Dabinon Awansu da Mandawari
Da Alfindiki Kwalwa duk a Kano

Tsaya in gajarta guda don kau yawaita
In kawo wurinta da niyyi Kano

Fa har muka kare naje Nasarawa
Garin makarantan su Sambon Kano

Akwai makaranta karatun Bature
Acan Nasarawa ta kofar Kano

akwai yara masu Karatu na allo
Akwai masallaci ginanne Kano

AKwai Makaranta ta al Kur'ani
Da litattafanmu a birnin Kano

Akwai wani dakin zaman masu ciwo
Akwai matsarinsu a kofan Kano

Masaka, madunka, da mai Sassaka
Gidansu guda makarantan Kano

Makera, Badukai da masu kudi
Cikin makaranta ta kofar Kano

Cikin shekara goma sha dai ga daula
Aliyu binu Sidi zuwanshi Kano

Ya wake ta yan baya domin su ji
Su san wakacin tafiyanshi Kano.

Dadadan Dadin Saniya; Daga Dr Aliyu Aqilu

Malam Aliyu Aqilu dai ba bako bane ga wanda yasan wakokin Hausa. Asalinsa mutumin Sakkwato ne, duk da yake a Kano yafi shahara, kuma anan iyalinsa suke, ana kuma Allah yayi masa rasuwa. An haife shi a shekara 1918, a garin Jega na kasar Gwandu, wanda a yanzu ke jihar Kebbi. Cikin malaman da yayi karatun alqur'ani a gunsu sun hada da ; mahaifinsa Aliyu Madaha, da kuma Alhaji Muhtar Tsoho, da Malam Muhammadu dan Takusa, da M Ban-Allah, da kuma malam AbdulMumini. Ya fara zuwa Kano tun yana da kamar shekaru 15, babban malaminsa a Kano shine: Malam Mahmudu na malam Salga, kuma Muqaddaminsa na Tijjaniya shine Malam Salga. Ya zauna a Borno shekara 23. Malam Akilu Aliyu gogaggen dan siyasa ne, kuma mai bin akidun siyasar NEPU, kuma sana'ar da aka fi saninsa da ita, itace dinki. Ya samu Digirin girmamawa (Honorary Doctorate Degree) daga Jamiar Bayero ta Kano, kafin rasuwarsa. Ya wallafi wakoki da dama, cikinsu kuwa sun hada da na addini, siyasa, zaman tare, tafiye-tafiye dss. To acikinsu ne na zabo mana daya daga ciki, kafin in Allah ya yarda mu kawo muku sauran, wannan waka kuwa itace wadda fasihin Sha'irin yayiwa Saniya. Ga dai wakar;

Ya mai ni'ima mayawaiciya
Ya mai kudura makadaiciya

Haske da basira naka ne
Ya Rabbu ka buden zuciya

Domin inyi waka yar kadan
Mai yar magana mashahuriya

Amma a takaice a dan mu san
Dimbin amfanin Saniya

Sunce mata dadi goma wai
Wannan magana na dai jiya

Wato maganar na ji ta ne
Karba tata sai na waiwaya

A'a karbarta da lokaci
Sai na juya na waiwaya

Ba goma bama wane dari
Metan suke har da guda daya

Wa za shi iya shi kididdige
Dadadan dadin Saniya

Nan dai a takaice guda darin
Zan zo muku yanzu da dai daya

To sai muyi tsit domin mu ji
Zan fara bayanin Saniya

Mamaki ne da tu'ajjibi
acikin sha'anonin saniya

Tirkashi! O'oi, wane mutum
Sanbarka dau duka saniya

Kin dau kaya kin dau mutum,
Da abinci mutum ya rataya

Kallonta shi sanya farinciki
Kukanta shi sanyaya zuciya

Shafarta shi sa maka walwala
Dubarta idonka shi sanyaya

Ba'a samu guda ba na yasuwa
Daga kowane sashin saniya

Madara, Kindirmo, Dakkashi
Kangar da Cukui daga Saniya

Kassanta ana Alli dasu
Ya kyautu anan in waiwaya

Kashinta ana shafe dashi
Losonmu na da Nijeriya

Kirginta ana wasaki da shi
Mun san haka duk Nijeriya

Har gobe ana kiri da shi
Da gareshi ake bulaliya

Na lura ana Waga dashi
Da gareshi ake yin tsirkiya

Shike daure karaga da shi
Tsani, Barho da Takobiya

shike yin takalma da shi
Kwakkwaran kirgin Saniya

Na lura da shi ke yin kube
Na wuka, Barho da Takobiya

Ka tuna fa da shi ke Janjami
Sai mai girma kan rataya

Baza na yawaita maganganu
Ga yar sa'at magajarciya

Ba nuna gadara ko isa
Ko kasaita matsananciya

Daga nan ya zuwa can ko ina
Acikin duka sassan duniya

Na hanga, zaune a hankali
Kuma na maka duba na tsaya

Wai ko zan gano na yasuwa
Wani dan gutsure daga Saniya

Anya kuwa a same shi dai?
Amsa naka so na tambaya

Shin ko ko akwai abu ne daban
Marashin fa'ida daga saniya

Indai da akwai a fada muji
Daga Sa ya zuwa kan Saniya

Guzuma ta zamo ko Dangwala
Ko Karsana ce ma Sauraya

Amsa a'a ai babu shi
Abu yasasshe daga Saniya

Wannan kuwa ta gamsar da ni
Amsa ke nan makatarciya

Mai haske gata a wartsake
Har yau mai dada zuciya

Wakar sunan dana bata shi
Dadadan dadin Saniya

Wannan jin dadin ya isa
Daga kowane sashin Duniya

Kar wai ku cane gefe guda
Daga kowane barin kun jiya

Me zamu kwatanta ne da shi
Ga misali, sai dai lafiya

Wannan itace duk kan gaba
Daga duk jin dadin duniya

Amma a wadata kowace
Daga kowane fannin duniya

Jama'u-Jama'u duk an hadu
Cewa dai babu ya saniya

Fifiko nata yana gaba
ga na dabbobi duka saniya

Yai nisa basu tara da shi
Ko sunyi gudu sun garzaya

Ba za fa su shawo kan sa ba
Ko sun zaga sun kewaya

Kai ban zaci sa riske shi ba
Ko sun tafiya matsananciya

Abu ne mawuyaci dankari!
Har yanzu wuyar mawuyaciya

Gaba dai, gaba dai, gaba dai, gaba
Gaba, Nagge, da aiki saniya

Ja al'amarinki madaukaki
Gaba dai ba baya ba Saniya

Ja dai sha'aninki na arziki
Ke baki shiga sha'anin tsiya

Madalla, madalla dake
Tsarinki da kyawo saniya

Sannunki nace na gaida ke
ni na yabi aikin saniya

Girman daraja, girman isa
Sannan darajar mayawaiciya

Taure yace a sanar dake
sakon akuya da na Tunkiya

Sun mika wuya sun sallama
Cewa a nada ki sarauniya

Sun sa hannu da guda-guda
Sun lamunce daga zuciya

Rago tuni shi ya sallama
Dauke shi jakada saniya

Dabbar da ta ja gaba dake
Ta dau wahala matsananciya

Gurbin riba sai faduwa
Sai rarraba hajjar mujiya

Tsini akaje nema gaba
Kunda ta gagara tun jiya

Wannan magana bata fadi ba
Wa zaya gaya mini "Kai tsaye"

Jama'a daga nan zan dakata
In sanya alama in tsaya

Ni naku Aliyu Aqilu ne
amsa a wajen maitambaya.